Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Wasu jihohin Najeriya za su yi asarar Dala Miliyan 700 na kudaden tallafi daga bankin CBN

Published

on

Wasu daga cikin jihohin kasar nan ba za su sami Dala Miliyan dari 700 na kudaden tallafi daga bankin kasar nan in har suka gaza buga kasafin kudin su na badi a kafar Internet daga nan zuwa watan Fabarerun badi.

Babban daraktan hukumar hadi gwiwa na gwamnatoci na jihar Niger Alhaji Sirajo Sai’d ya bayyana hakan a yayin taron hadin gwaiwa da hukumar da kuma kungiyoyin kishin al’umma da aka yi a birnin Minnan jihar Naija.

A cewar Ahaji Sirajo Sa’id ya ce tallafin kudaden wanda zai zo karkashin shirin fayyace gaskiya kan tattalin arziki da kudi da kuma dorewar cigaban ayyukan wanda gwamnatin tarayya ta karba a madadin gwamnatocin jihohin kasar nan.

Babban darktan hukumar ta hadin gwiwar gwamnatocin na jihar Niger ya kara da cewar, makasudun baiwa gwamnatocin tallafin kudaden da bankin duniya zata yi shi ne don tabbatar da ayyukan al’umma da tsage gaskiya wajen kashe kudade don cigaban ‘yan Najeriya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!