Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

WHO ta ja hankali kan cutar daji

Published

on

Hukumar lafiya ta duniya ta bukaci gwamnatoci da su inganta cibiyoyin lafiya a kasashe masu tasowa da wadanda suka cigaba.

Hukumar lafiya ta bayyana haka ne a wata sanarwa da ta wallafawa a shafita a yayin da ake gudanar da bikin ranar cutar daji ta duniya da ake gudanarwa a duk ranar 4 ga watan Fabrairun kowacce shekara.

Hukumar ta WHO ta gargadi kasashe da cewar muddin ba’a shawo kan cutar daji ba, nan da dan lokaci zai karu da kimanin kaso 60 cikin dari.

Sanarwa ta kara da cewa za’a samu wannan kari na masu cutar ne da kaso 81 cikin dari a kasashe masu tasowa inda ko a yanzu wadanda suke dauke da cutar ke shan wahalar samun sauki daga cutar daji.

Mataimakin darakta a hukumar wanda yake kula da bangaren samar da lafiya da cutuka masu yaduwa da wadanda basa yaduwa Dr Ren Minghui  ya ce wannan kididdiga yunkuri ne na  zaburar da kasashe domin shawo kan matsalar cutar daji.

Inda ya ce da zarar an  samarwa al’umma cibiyar lafiya da za’a dinga kai marasa lafiya , hakan zai taimaka wajen gano cutar da akan lokaci .

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!