Connect with us

Labarai

INEC ta amince da David Mark a matsayin shugaban jam’iyyar ADC na ƙasa

Published

on

 

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya ta amince da jagorancin jam’iyyar ƴan haɗaka ta ADC, ƙarƙashin shugabancin tsohon shugaban Majalisar Dattijan Najeriya, David Mark

 

Hukumar zaɓen ta yi hakan ne bayan wallafa sunan shugabannin jam’iyyar a shafinta na intanet.

 

Hakan na zuwa ne bayan fafutikar da haɗakar ƴan’adawa na ƙasar ke yi wajen ganin sun yi abin da suka kira “inganta jam’iyyar” domin tunkarar babban zaɓen ƙasar na shekara ta 2027.

 

A ranar 2 ga watan Yulin wannan shekara ne haɗakar ƴan hamayyar siyasa na Najeriya suka ayyana ADC a matsayin jam’iyyar da za su yi amfani da ita, tare da bayyana Sanata David Mark da Rauf Aregbesola a matsayin shugaba da kuma sakataren jam’iyyar na ƙasa.

 

Sai dai duk da haka an shafe tsawon lokaci babu sunan sabbin shugabannin da aka ayyana a shafin na hukumar Inec.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!