Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yajin aikin ƴan adaidaita sahu: hukuncin KAROTA ya saɓa doka – Barista Abba Hikima

Published

on

Wani lauya me zaman kansa anan Kano ya ce, hukuncin da hukumar KAROTA ta yi ga matuƙa baburan a daidaita sahu na biyan kudin haraji duk shekara ya saɓa da tsarin doka.

Barista Abba Hikima Fagge ne ya bayyana hakan a zantawarsa da Nasir Salisu Zango ranar Litinin.

Lauyan ya ce, duk da dokoki sun bai wa hukumar KAROTA dama ta karɓi haraji ko kuma ta bada lasisin tuƙi amma babu inda doka ta ce duk shekara sai sun biya kuɗi.

“Wannan abu bai dace ba, duba da yadda ake fama da matsin tattalin arziƙi Wanda yin hakan na iya kawo musu naƙasu a cikin harkar kasuwancin su”.

Baresta Abba Hikima Fagge ya kuma ce, dokar na magana ne akan idan matuka baburan sun biya sau ɗaya ya wadatar, la’akari da yadda baburin baya daɗewa kuma ba wani abu suke samu sosai ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!