Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

‘Yan gudun hijira sun gudanar da zanga-zanga sakamakon yunwa da ta addabe su

Published

on

A jiya Taalata ne dubban ‘yan gudun hijira da ke Baga a garin Maidugurin Jihar Borno suka mamaye manyan titinan dake garin domin nuna damuwar su bisa rashin kayan abinci da suke fuskanta.

Haka kuma rahotonni sun yi nuni da cewa zanga zangar ta hadar da rashin magunguna da kulawa da basa samu a yayin da basu da lafiya a sansanin da suke zaune.

Masu zanga zangar sun rufe wasu manyan tituna a garin na Maiduguri da suka hadar da babban titin Maiduguri zuwa Kano da sauran wasu muhimman hanyoyi.

Zanga-zangar ta hadar da mata da kananan yara maza da mata da maza da suka fito dauke da kwalaye dake dauke da rubutu da ke nuna irin matsalar da suke fuskanta tare da rera wakoki na irin matsalolin da ke damun su.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!