Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ministan kasafi:Ana sa ran tattalin arzikin Najeriya zai karu da sama da kashi 3

Published

on

Ministan kasafin kudi  da tsare-tsare na Najeriya, Udoma Udo Udoma ya ce, akwai yiwuwar tattalin arzikin kasar zai karu da fiye da kashi uku a bana kamar yanda  wani rahoton Asusun bayar da  lamuni na duniya, IMF ya fitar.

Udo Udoma ya ce rahoton da IMF ya fitar Ya bayyana yanda tattalin arzikin kasar nan a watan junairun da ya gabata ya yi sama musamman ta bangaren kasuwar danyen mai  ya karu da sama da Kashi biyu.

 Udoma ya kara da cewa   Ana saran kasafin kudin bana zai habaka tattalin arzikin kasar nan tare da samarwa  matasan ayyukan yi a kasar nan, baya ga ragewa da yawa daga cikin al’umma halin matsin da suke ciki.

A cewar Minista Udo udoma a dadin da ake sa ran za’a samu ya kai sama da kaso tara a shekarar nan, daga cikin kaso goma sha daya hkamar yadda yake a karshen shekarar 2018.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!