Labarai
Yan kasuwar sayar da wayoyi ta Unguwa Uku sun nemi daukin gwamnatin Kano

Wasu daga Cikin yan kasuwar sayar da wayoyin hannu ta Unguwa Uku wato GSM Market sun koka akan yanda suke zargin shugabancin kasuwar da yi musu Mulkin Kama Karya harda Cin zarafin wasu daga cikin yan kasuwar.
A zantawar wasu daga cikin yan kasuwar da Freedom Radiyo sun ce, sun dade suna bukatar sauyin shugabancin a kasuwar saboda rashin adalcin da ake nuna musu,
Har ma suka kara da cewa tsawon shekara sama da goma kenan shugaban kasuwar yana kai kuma yaki bari ayi zabe, tare da hada kai da wani tsohon jami’in Dansanda har takai ga kotu ta aike da wasu daga Cikin yan kasuwar Gidan ajiya da Gyaran hali.
A nasa bangaren shugaban Kungiyar Kasuwar sayar da wayoyin hannu ta Unguwa Uku GSM Market Aliyu Abubakar Umar ya Magantu, inda yace wadanda akai kara kotu suna tada tarzoma ne acikin kasuwa hakan ce tasa aka hada su da hukuma har akayi musu Hukunci daidai da abinda suka aikata.
You must be logged in to post a comment Login