Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

‘yan Najeriya na ci gaba da dakon sakamakon zaben shugabancin kasa da na yan majalisu

Published

on

A yayin da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC za ta fara tattara sakamako zabe a yau yan Najeriya na ci gaba da dakon sakamakon zaben shugabancin kasa da na yan majalisu da aka kada tun a ranar Asabar din da ta gabata.

A cewar hukumar zaben da misalin karfe 11 na safiyar yau Litinin ne za a fara sanar da sakamakon zabukan shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya a hukumance.

Yayin da hukumar ta INEC ke cigaba da aikin tattara sakamakon zabukan da aka gudanar, a jiya Lahadi an bai wa jama’a damar kada kuri’unsu a wasu mazabu da ke kananan hukumomi 10 na jihar Zamfara, inda jama’a suka kasa yin zaben a ranar Asabar.

Haka kuma INEC ta ce za ta bayyana sabbin ranakun da za a sake gudanar da zabukan shugaban kasa da na ‘yan majalisar wakilai da dattijai, a wasu yankuna na jihohin Anambra da Rivers da Lagos sakamakon rikicin da aka samu da kuma sace akwatinan zabe.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!