Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

INEC:ta kori mai tattara sakamakon zaben karamar hukumar Bokkos dake jihar Filato

Published

on

Hukumar zaben mai zaman kanta ta kasa INEC ta kori Farfesa Musa Izam a matsayin mai tattara sakamakon zabe a karamar hukumar Bokkos dake jihar filato 

Rahotanni sin yi nuni da cewa Izam wanda malamin komiyya ne a jami’ar Jos ya yi yunkurin gujewa sanar da sakamakon zaben karamar hukumar, sai dai matasan da ke yankin suka iza keyarsa zuwa cikin hukumar suka hanashi guduwa.

A cewar jami’in hukumar ta INEC a jihar ta Filato Mista Osaretin Imahiyerobo, ya zama wajibi su kori farfesan sakamakon buguwa da yayi a dalilin shaye-shaye da ya hana shi ci gaba da gudanar da aikin nasa.

Ya kuma ce hukumar ta INEC za ta dauki matakin gaggawa domin ganin ba a saamu matsala wajen tattara sakamakon zaben a yankin ba.

 Ya kuma ce suna jaran farfesan ya dawo garin Jos ya kuma yi musu bayanin dalilan dasuka sanyashi ya yi wannan danyen aiki kafin daukar mataki na gaba.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!