Connect with us

Labarai

Yan Najeriya na da damar neman daukin kasashen waje kan matsalar tsaro – Obasanjo

Published

on

Tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya ce ’yan Nijeriya na da cikakken ’yancin neman taimakon kasashen waje idan gwamnatin Nijeriya ta gaza kare rayukansu.

 

Obasanjo ya yi jawabin ne yayin wani taron Kirsimeti a Jos, inda ya ce bai kamata a ji kunyar neman taimako ba idan gwamnati ta kasa cika babban nauyinta na tsaro.

 

channels TV ta ruwaito Obasanjo ya ce a zamanin da ake amfani da tauraron dan adam da jiragen sintiri, bai kamata ’yan ta’adda su rika kashe mutane su bace ba. Ya zargi gwamnati da gazawa, yana mai cewa hare-hare da kashe-kashe sun yi yawa, kuma ’yan kasa sun gaji da zubar da jini.

 

Hakazalika, ya tuna da sace ’yan matan Chibok, yana mai cewa matsalar tsaro ta kara tabarbarewa maimakon ta inganta, kuma ya jaddada cewa kariyar ’yan kasa ita ce aikin farko na kowace gwamnati, amma a halin yanzu gwamnati ba ta iya kare al’umma yadda ya kamata ba

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!