Labarai
Yan Sandan Burtaniya na shirin tsaurara tsaro yayin ziyarar shugaba Tinubu

Mahukuntan Birtaniya sun sanar da cewa za a ɗauki tsauraran matakan tsaro a garin Windsor yayin ziyarar aiki da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai kai ƙasar.
A wata sanarwa da rundunar ƴan sandan Thames Valley ta fitar, ta ce za a rufe wasu hanyoyi tare da faɗaɗa dokar hana zirga-zirgar jiragen sama a sararin samaniyar Windsor a ranar 18 ga watan Maris.
Ana sa ran shugaban zai isa tare da matarsa Oluremi Tinubu, inda King Charles III zai karɓe su a Windsor Castle domin gudanar da liyafar girmamawa.
Jami’an tsaro sun ce matakan da ake ɗauka na daga cikin shirye-shiryen tabbatar da tsaro yayin ziyarar shugaban Najeriya a ƙasar.
You must be logged in to post a comment Login