Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yanzu-yanzu: Majalisar dokoki ta amince Ganduje ya ciyo bashin Naira Biliyan 10

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano, ta amincewa gwamna Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya ciyo bashin naira biliyan goma.

Kuɗaɗen da za a ciyo bashin, za a yi amfani da su wajen sanya na’urorin CCTV domin kyautata tsaro a jihar.

Amincewar ciyo bashin ta biyo bayan wasiƙar da gwamnan ya aikewa majalisar wadda shugabanta Injiniya Hamisu Ibrahim Chidari ya karanta a zaman majalisar na ranar Laraba.

Ta cikin wasiƙar gwamna Ganduje ya ce, za a sanya na’urorin ne la’akari da barazanar tsaro da jihar ke fuskanta a ƴan kwanakinnan.

Wakilin Freedom Radio a majalisar Auwal Hassan Fagge ya ruwaito cewa, bayan tattauna batun ne tare da bada shawarwari ƴan majalisar suka amince a ciyo bashin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!