Connect with us

Labarai

Yau za’a tantance Christopher Musa mai ritaya  a matsayin sabon Ministan Tsaro a Najeiya

Published

on

Majalisar Dattawan Najeriya ta bayyana yau Laraba, 3 ga Disamba, 2025, a matsayin ranar da za’a tantance Janar Christopher Gwabin Musa mai ritaya  a matsayin sabon Ministan Tsaro, bayan murabus ɗin Alhaji Mohammed Badaru Abubakar.

 

Ta cikin sanarwar da Sanata Opeyemi Bamidele, ya ce sun karɓi bukatar Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu don gaggauta tabbatar da sabon ministan.

 

Bamidele ya bayyana cewa ba za a jinkirta wannan bukata ba saboda halin da tsaron kasa ke ciki, inda ake bukatar haɗin kan majalisa da fadar shugaban kasa. 

 

Janar Musa, wanda ya sauka daga mukamin sa na shugaban Sojin kasar nan  kusan makonni biyar da suka gabata, ya samu wannan amincewar shugaban kasa  bisa kwarewa da cancanta a fannin tsaro.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!