Connect with us

Kasuwanci

Za mu gina kasuwannin sayar da Gwal da ta sayar da Magungunan Gargajiya- Gwamnatin Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce, za ta gina wasu sabbin kasuwanni guda biyu da suka hada da kasuwar sayar da Gwalagwalai zalla da kasuwar sayar da Magungunan gargajiya.

‎Kwamishinan harkokin kasuwanci da zuba Jari na Kano, Alhaji Shehu Wada Sagagi ne ya bayyana hakan yau a taron rantsar da sabbin shuwagabannin Cibiyar Kasuwanci ta Kano KACCIMA da aka gudanar.

 

Haka kuma kwamishinan, ya ce, gwamnatin Kano za ta hada kai da cibiyar ta KACCIMA domin ganin harkokin kasuwanci sun bunƙasa a faɗin jihar Kano.


‎Ambasada Usman Hamza Darma shi ne sabon shugaban Cibiyar ta KACCIMA, ya ce, za su duba kowanne bangare na harkokin kasuwanci a fadin jihar Kano domin ganin sun kawo gyare-gyaren da za su bunkasa harkokin kasuwanci.

‎A nasa bangaren Alhaji Ado Muhammad wanda ya jagoranci kwamitin gudanar da zabe na Maslaha a Cibiyar ta KACCIMA ya yi wa sabbin shugabannin fatan nasara a bisa jagorancin da suka karba tare da yi musu addu’ar samun nasara.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!