Connect with us

Labarai

Za mu hada kai da Turkiyya domin yakar rashin tsaro – Tinubu

Published

on

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa gwamnatinsa ta nemi taimakon kasar Turkiyya wajen yakar matsalar tsaro da ke addabar wasu sassan Nijeriya.

 

Tinubu ya bayyana haka ne a ranar Juma’a yayin tattaunawa da wata tawagar kungiyar Kiristoci ta Nijeriya a gidansa da ke jihar Legas.

 

 

Sanarwar da hadiminsa Bayo Onanuga ya fitar, ta ce ya bukaci samun hadin kai daga kungiyar, musamman wajen hakuri da kuma fahimtar irin matakan da gwamnatinsa ke dauka.

 

Kazalika ya jaddada kudurin kafa ‘yansandan jihohi, a daidai lokacin da gwamnati ke kan aikin hadin gwiwa da kasar Amurka wajen yakar matsalar tsaro, kamar yadda gidan Talabijin na Channels TV ya ruwaito.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!