Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Za mu sauya tunanin matasan Kano daga shaye-shaye da ayyukan daba- Dr. Abubakar

Published

on

Kwalejin fasaha ta Kano, ta sha alwashin tallafa wa harkar yaƙi da shaye-shayen miyagun ƙwayoyi, da ayyukan daba a fadin jihar.

Shugaban kwalejin Dakta Abubakar Umar Faruk, ne ya bayyana hakan a yayin tattaunawa da manema labarai a ofishin sa.

Ya ce, kwalejin ta Kano Poly ta duƙufa wajen koyar da matasa maza da mata sana’o’in da za su dogaro da kan su bayan kammala karatu.

Dakta Abubakar ya ƙara da cewa matuƙar al’umma za su rungumi ilimin fasaha a matsayin hanyar samun aikin yi, to kuwa za a rage yawan aikata laifuka a jihar Kano da ma kasa baƙi ɗaya.

Daga nan sai ya buƙaci ƴan kasuwa da masu sana’ar hannu a faɗin jihar Kano da sauran jihohin ƙasar nan da su fito da tsare-tsare da don cin gajiyar duk wani tallafi da gwamnati da ƙungiyoyin agaji ke bayarwa.

Kamar yadda sanarwar da jami’in hulɗa da jama’a na kwalejin Auwal Isma’il Ɓagwai ya fitar ta bayyana.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!