Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Za’a gudanar da tsaftar muhalli na karshen watan nan – Kabiru Getso

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci al’ummar jihar da su yi amfani da ranakun juma’a da asabar na karshen wata wajen tsaftace muhallan su musamman a wannan lokaci na damuna a wani mataki na magance matsalar ambaliyar ruwa.

Kwamishinan muhalli na jihar Kano Dr Kabiru Ibrahim Getso ne ya bayyana hakan a yau, ta cikin sanarwa mai dauke da sa hannun mai magana da yawun ma’aikatar Abbas Habib Abbas jim kadan bayan kammala ganawa da masu ruwa da tsaki don yin shirye shiryen zagayen tsaftar muhalli da za a gudanar a karshen watannan.

Yace, zagayen tsaftar muhalli an dakatar da shi tsawon lokaci sakamakon annobar Corona wadda da shafi al’amuran rayuwar yau da kullum.

Dr Kabiru Ibrahim Getso ya Kara da cewa sai dai a waccan lokaci gwamanati tayo amfani da damar ta wajen gudanar da feshin maganin kariya daga cutar corona a makarantu da tashoshi da kasuwanni da nasallatai da sauran guraren ibada.

Yana Mai cewa a yanzu ma’aikatar muhalli ta shirya gudanar da zagayen tsaftar muhalli a gobe jumaa a wasu daga cikin kasuwannin jihar sai Kuma ranar asabar da za a gudanar da tsaftar titina da sauran unguwanni.

Dr Getso ya bukaci jamaar jihar Kano su bada hadin Kai daga karfe bakwai na safe zuwa goma na safiyar ranakun jumaa da asabar don tsaftace muhallin su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!