Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Za’a hukunta wadanda ke da hannu a rikicin Filato

Published

on

Gwamnan Jihar Filato Simon Lalong ya ce mutanen da aka kama kan zargin hannu cikin rikicin da ya wakana a Jihar kwanan nan da ya yi sanadyyar asarar rayuka da dukiyoyi, za su fuskanci Shari’a ne a garin Jos sabanin yadda aka saba gudanar da makamanciyar Shari’ar a birnin tarayya Abuja.

Lalong na bada wannan tabbaci ne lokacin da ya karbi wata kungiyar Kiristoci a fadarsa domin jajanta ma sa kan al’amarin da ke wakana a Jihar.

Gwamna Lalonga ya shaida wa kungiyar irin matakan da aka dauka na kawo karshen tashe-tashen hankula a Jihar, tare da tabbatar da wanzuwar zaman lafiya a Jihar da ma kasa baki-daya.

Shugaban kungiyar Pentacostal Fellowship Rabaran Felix Omobunde ya tir da al’amuran da suka faru na kasha-kashe, sannan ya bukaci a kama duk masu hannu a ciki sannan a yi mu su Shari’a a Jihar ta Filato.

 

 

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!