Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Gwamnatin Kano ta sha alwashin kammala ayyukan da ta gaba

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta jaddada kudurinta na kammala ayyukan da ta faro a sassa daban-daban na fadin Jihar nan.

Kwamishinan ayyuka Sufuri da Gidaje na Jihar Kano Injiniya Aminu Aliyu Wudil ne ya bayyana hakan yayin rangadin duba ayyukan da ake tsaka da gudanarwa a halin yanzu.

hanyoyin dai sun hada da gyaran Titin Kofar Waika daura da gidan zakka, da ginin dakunan karatu da zai dauki adadin dalibai 1500 a mazaunin din-din na Jami’ar Yusuf Maitama Sule, da kuma aikin magance zaizayar kasa a Barikin Sojojin sama na nan Kano.

Ya ce akwai bukatar jama’a su ci gaba da bada hadin kai wajen ganin an samu nasarar kammala ayyukan, tare da bayar da kyakkyawar kulawa kan ayyukan da gwamnati ke yi.

Da yake jawabi kwamandan Barikin Sojin sama na 455 Air Commodore Idris Sani ya bayyana jin dadinsa, duba da yadda zaizayar kasa ke ci gaba da cinye sassan Barikin.

Wakilin mu Umar Idris Shu’aibu ya ruwaito cewa yayin kewayen Kwamishinan ayyuka Sufuri da gidajen Injiniya Aminu Aliyu Wudil ya duba sabbin gine-gine a Makarantar gwamnati da ke garin Dawakin Tofa da kuma ginin gidaje a kauyen Ganduje da ambaliyar ta ruguje.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!