Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za’a kammala aikin titan Badin ruwa Lagos a shekara ta 2021

Published

on

Kamfanin da ke aikin gina babbar hanyar  garin Badin zuwa Lagos ya ba da tabbacin kammala aikin Titin daga nan zuwa shekarar 2021.

Babban jami’in gudanawar Kamfanin Thamm Olaf ne ya shaida hakan lokacin da yake bada ba’asi a gaban Kwamitin ayyuka na Majalisar Dattijai a jiya Lahadi.

Ya kara da cewa sun gaza kammala aikin a shekarar da ta gabata kamar yadda aka tsara sakamakon karancin kudade, da kuma sake fadada aikin da aka yi.

Yayin ziyarar gani da ido da Kwamitin ya kai wuraren da ake aikin a Jihar Lagos karkashin shugabansa Sanata Kabiru Ibrahim Gaya, ya bayyana rashin jin dadinsa duk kuwa da makudan kudaden da gwamnatin ta narka cikin aikin ginin Titin.

Sanata Kabiru Ibrahim Gaya ya shaidawa manema labarai cewa Kamfanin da ke aikin wurin ajiye mayan Motoci na Tin Can Island ya sanar da su cewa zai kammala a cikin Disamba mai kamawa, don saukaka cunkokson ababen hawa da ake samu.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!