Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Za’a tilastawa ma’aikatan gwamnati amfani da jirgin Nigerian air da zarar an kaddamar da ita

Published

on

A kokarinta na ganin an bunkasa harkokin Sufurin Jirgin saman kasar nan gwamnatin tarayya ta sanar da fara wani yunkuri na tilastawa ma’aikatanta tafiye-tafiye ta sabon kamfanin da aka kaddamar na kasa Nigeria Air.

Karamin Ministan Sufurin Jiragen sama Hadi Sirika ya ce gwamnatin tarayya ganin Majalisun tarayya sun yi dokar da za ta tilasta hakan don ganin komai ya tafi yadda aka tsara.

Ministan ya bayyana cewa ba didai ba ne yadda wasu ke cece-ku-ce da takaddama dangane da inganci da kuma ‘yancin sunan kamfanin, kamar yadda wasu ke muhawara a kai a shafukan zumunta na zamani.

Ya kuma kara da cewa batun yarjejeniyar da gwamnatin ta kulla da ‘yan kasuwa abu ne mai kyau da zai haifar da ‘da mai ido cikin kankanin lokaci matukar harkokin suka kankama.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!