Connect with us

Labarai

Zan koma Majalisa ranar Talata- Sanata Natasha

Published

on

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta bayyana cewa za ta koma majalisar dattijai a gobe Talata, bayan hukuncin kotu da ya soke dakatarwar da aka yi mata.

 

A wani bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta, Sanatar ta gode wa magoya bayanta bisa jajircewarsu, tana mai cewa wannan hukunci babbar nasara ce ga dimokuraɗiyya.

 

A cewar babbar kotun tarayya da ke Abuja, dakatarwar da majalisar ta yi mata ta sabawa kundin tsarin mulki, kuma ta tauye ‘yancin wakilcin jama’arta. Kotun ta umarci a dawo da ita bakin aikinta nan take.

 

Sai dai kotun ta ci tarar Sanatar Akpoti-Uduaghan Naira milyan Biyar, saboda kin bin umarnin da aka bayar a baya. Wannan ya biyo bayan wani rubutu da ta wallafa a shafinta na Facebook, duk da cewa kotun ta haramta mata yin hakan a baya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!