Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Zargin almundahana: Kotu ta bada umarnin a kamo jarumi Sadik Sani Sadik

Published

on

Wata Kotu a nan Kano ta Umarci ɗan Sandan Kotu daya kamo Mata jarumin wasan kwaikwayon nan Sadik Sani Sadik.

Kotun shari’ar musulunci da ke Zamanta a Hotoro masallaci ƙarƙashin mai shari’a Sagir Adamu ce ta bada umarnin kamo Sadik ɗin sakamakon bijirewa umarnin ta.

Tunda fari dai wani mashiryin Film ne wato Aliyu Adamu Hanas yai ƙarar sa sakamakon bashi kafin alƙalamin kuɗin aiki shirin wasan kwaikwayo shi kuma bai yi aikin ba kuma ake zargin ya hana shi kudin hakan yasa ya garzaya kotun domin roƙon ta nemar masa haƙƙin sa.

Kotun dai ta aike da sammaci amma ba a same shi ba ta kuma bada umarnin a liƙe masa takardar a gidansa da ke Tudun Yola amma har yanzu bai bayyana ba.

Wakilin Freedom Radio Aminu Abdu Baka Noma ya rawaito cewar me ƙara yana neman Naira dubu tamanin a hannun Sadik ɗin kuma zai sake shigar da ƙara ta neman haƙƙin sa na ɓata masa lokaci da kuma jawo masa asara sakamakon rashin halartar aikin da yayi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!