Connect with us

Labarai

Zauren Majalisar Dokoki ya dade ya bukatar gyara – Ahmad Lawan

Published

on

Shugaban majalisar dattijai Ahmad Lawan ya ce zauren majalisar dokoki ta kasa na bukatar gyare-gyare tun ba yanzu ba.

Lawan ya bayyana haka ne bayan da mataimakin mai tsawatarwa na majalisar dattawa Sanata Aliyu Sabi Abdullahi ya gabatar da bukatar gyara zauren majalisar dokokin.

Sanata Abdullahi ya ce, akwai kura-kurai sosai a yawancin rahotannin dake yawo a shafukan sada zumanta kan batun yoyo tare da mamaye zauren majalisar da ruwan sama yayi.

Ya kuma ce lamarin zai haifar da zubewar mutuncin ‘yan majalisar a idanun ‘yan Najeriya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!