Labarai
Ƙudurin gyaran dokar ofishin mai binciken kuɗi na Kano ya tsallake karatu na biyu

Ƙudurin gyaran dokar ofishin mai binciken kuɗi na baɗi na jihar Kano, ya tsallake karatu na biyu a zauren Majalisar dokoki ta jiha.
Ƙudurin dai ya kai wannan mataki ne a zaman majalisar na yau Talata bayan da shugaban masu rinjaye na majalisar Alhaji Labaran Abdul Madari wakilin ƙaramar hukumar Warawa ya gabatar da karatun na biyu.
A Litinin ɗin makon jiya ne dai akawun majalisar Alhaji Garba Baƙo Gezawa, ya gabatar da karatu na ɗaya na dokar.
Za mu kawo muku cikakken labarin a nan gaba.
You must be logged in to post a comment Login