Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ƙudurin dokar kasafin kuɗin baɗi ya tsallake karatu na biyu

Published

on

Ƙudurin dokar kasafin kuɗin baɗi, da gwamna Injiniya Abba Kabir Yusuf ya gabatar, ya tsallake karatu na biyu a zauren majalisar dokokin jihar Kano.

Ƙudurin ya kai wannan mataki ne bayan da mambobin majalisar suka amince da karatun na biyu wanda shugaban masu rinjaye na zauren Alhaji Lawan Hussaini Chediyar ƴan Gurasa ya gabatar yayin zaman majalisar na yau Litinin ƙarƙashin jagorancin shugaban majalisar Alhaji Jibril Isma’il Falgore.

Bayan amincewa da ƙaratun, majalisar ta kuma bai wa kwamitinta na harkokin kasafi tsawon makonni uku da ya gudanar da aikin kare kasafin ga ma’aikatu da hukumomin gwamnati tare da gabatar da rahoto.

Wannan dai na zuwa ne bayan da aka buɗe majalisar daga yajin aikin da ƙungiyar ma’aikatan majalisun jihohin ƙasar nan suka yi na fiye da makonni uku.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!