Labarai
Ƙungiyar Hezbollah ta kai hari sansanonin sojin Isra’ila uku

Ƙungiyar Hezbollah mai samun goyon bayan Iran ta bayyana cewa ta kai hari kan sansanonin sojin Isra’ila uku a matsayin martani ga barnar da harin Isra’ila ta yi wanda ya shafi garuruwa da ƙauyuka da dama a Lebanon.
A cikin saƙonni guda uku da ta wallafa a shafin Telegram, Hezbollah ta ce ta harbi sansanin Nafah dake kan tsaunukan Golan da manyan roka, sannan ta kuma kai hari kan sansanonin jiragen sama na Meron da Ramat David, a arewacin Isra’ila da jirage marasa matuƙa.
Isra’ila ba ta yi wani bayani ba game da harin da Hezbollah ta ce ta kai mata.
You must be logged in to post a comment Login