Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ƴan baro dake kasuwar sabon Gari sun gudanar da zanga-zanga

Published

on

Ƙungiyar ƴan baro dake kasuwar sabon gari anan kano sun gudanar da zanga-zangar lumana akan titin gidan Gwamnatin jihar, inda suke zargin shugabancin kasuwar da tilasta musu tashi daga guraren da suke gudanar da kasuwancin su a kasuwar, inda suka ce hakan na barazana da rayuwar su.

Shugaban ƙungiyar Tasi’u Ibrahim ne ya jagoranci zanga-zangar lumana a yau inda suke kira ga mahukunta wajen duba halin da zasu shiga idan har aka tilasta musu tashi a wannan lokaci.

Da yake jawabi jim kaɗan bayan zanga-zangar, Shugaban kasuwar ta sabon Gari Alhaji Abdul Bashir Hussain yace ba wai haka kawai aka ce su tashi ba sai da shugabancin kasuwa ya zauna, domin samar kyakkyawan tsari a cikin kasuwar.

Haka kuma la’akari da yadda kasuwar ta cunkushe ya sanya dole ayi tsarin da zai samar da rage cucewar kasuwar shiyasa aka dau wannan mataki, a cewar shugaban kasuwar.

Haka zalika shuagabancin kasuwar yace akwai tsarin da akayi musu wajen daina shigowa da baro cikin kasuwar domin rage cinkoson da yake a kasuwar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!