Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ɗan Sarauniya ya goyi bayan Baffa kan ƴan adaidaita sahu

Published

on

Tsohon Kwamishinan ayyuka na Gwamnatin Kano Engr. Mu’azu Magaji Ɗan Sarauniya ya goyi bayan hukumar KAROTA kan tilasta wa masu adaidaita biyan kuɗin haraji.

A cikin wani saƙon murya da ya aike wa Freedom Radio, Ɗan Sarauniya ya ce, abin da KAROTA ta yi daidai ne, kuma abu ne da ya dace a yi tun a baya.

Ya ce, bai ga abin ta da jijiyar wuya ga ƴan adaidaita ba, don kawai an ce su bayar da Naira ɗari-ɗari kullum.

Ya ƙara da cewa, ƴan adaidaita na amfani da tituna da tsaron jiha da lantarki na Gwamnati saboda haka babu dalilin da za su ƙi biyan wannan haraji.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!