Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Sojoji sun kashe sama da ƴan bindiga 394 cikin mako 3

Published

on

Shalkwatar tsaro ta ƙasa ta ce sama da ƴan bindiga 394 da ƴan ƙungiyar boko haram 85 ne sojoji suka kashe a wasu manyan ayyuka da suka gudanar cikin mako uku.

A cewar shalkwatar tsaron ta ce an samu nasarar kashe yan bindigar da suka addabi jihohin Borno Zamfara, Kaduna, Kano da kuma Taraba.

Mai magana da yawun rundunar tsaron Brigadier General Bernard Onyeuko ne ya bayyana hakan a zantawar sa da manema labarai a Abuja.

Onyeko ya kuma ce, rundunar ta gudanar da ayyuka na musamman tsakanin 2 ga watan Satumba zuwa 30 ga watan.

Ya ƙara da cewa, an kama sama da yan bindiga da yan fashin daji har ma da masu garkuwa da mutane ɗari da biyar, sai kuma sama da 2,783 da suka ajiye makaman su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!