Connect with us

Labarai

Jami’an KAROTA sun karbi horon bada agajin gaggawa

Published

on

Hukumar kula da zirga zirgar ababen hawa ta jihar Kano KAROTA, ta ce za ta fara yin amfani da sababbin dabarun zamani wajen fannin bayar da agajin gaggawa.

 

Shugaban hukumar Injiniya Faisal Mahmud Kabir, ne ya bayyana hakan a wajen taron bayar da horo kan dabarun bayar da agajin gaggawa ga jami’an hukumar ta hadin gwaiwa da sashen nazarin halayyar dan-Adam na jami’ar Bayero suka shirya.

 

A nata bangaren, Malama Rahama Sulaiman da ta kasance guda cikin masu bayar da horon ta ce, horon da jami’an na KAROTA suka samu zai kawo sauki wajen taimaka wa mutane da kuma gudanar da ayyukan hukumar.

 

Haka kuma, ta bukaci jami’an hukumar da suka samu horon da su yi amfani da shi ta hanyar da ta dace domin ceton rayukan al’umma a lokacin da wani iftila’i ya faru.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!