Connect with us

Labarai

Jam’iyyar APC ta sanya Aliko Dangote Femi Otedola cikin shawarwarin yakin neman zaben shugaba Buhari

Published

on

Jam’iyya mai mulki ta APC ta sanya fitattun ‘yan kasuwar nan Alhaji Aliko Dangote da kuma Femi Otedola cikin mambobin kwamitin bayar da shawarwari nay akin neman zaben shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Wannan na kunshe a wata sanarwa da mashawarcin shugaban kasa Muhammadu Buhari na musamman kan al’amuran yada labarai, Mr Femi Adesina ya fitar yau Juma’a a Abuja.

Sauran mambobin kwamitin sun hadar da mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo da jagoran jam’iyyar ta APC Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, da Sanata Ahmed Lawan, da Femi Gbajabiamila da kuma shugaban jam’iyyar APC na kasa Adams Oshiomole.

Ta cikin sanarwar Femi Adesina ya kuma bayyana cewa jam’iyya mai mulkin ta APC ta fitar da sunayen mutanen da za su kawo mata shawarwari kan yakin neman zaben, wanda shugaban kasa Muhammadu Buhari zai jagoranci kwamitin, yayinda Bola Tinubu kuma zai kasance shugaban kwamitin na biyu.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!