Labarai
APC za ta bai wa Shugaba Tinubu takardar shaidar nasara a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa

Jam’iyyar APC za ta bai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu takardar shaidar nasara da kuma tutar jam’iyyar a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a zaɓen shekarar 2027 a yau Lahadi.
Ta cikin wata sanarwa da Mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga ne ya fitar, ta ce kwamitin gudanar da zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa ne zai gabatar da takardar da tutar a wajen wani taro da za a gudanar a Cibiyar Taro ta Bola Ahmed Tinubu International Conference Centre da ke Abuja, bayan kammala tattara sakamakon zaɓen fidda gwani daga faɗin ƙasar nan.
Ana sa ran gwamnoni na jam’iyyar APC, mambobin Kwamitin Zartarwa na Ƙasa, Kwamitin Ayyuka na Ƙasa, mambobin Majalisar Dokoki ta Ƙasa da sauran manyan jiga-jigan jam’iyyar za su halarci taron.
You must be logged in to post a comment Login