Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Majalisar dokokin jihar Kano ta yadda da kara sarakunan yanka guda hudu

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta sahale ga gyaran dokar masarautu ta jihar Kano wadda ta amince da kafa sabbin Sarakunan yanka masu daraja ta daya a jihar ta Kano guda hudu.

Hakan ya biyo bayan amincewa da sakamakon rahoton da shugaban masu rinjaye na majalisar Baffa Babba Dan-Agundi ya karanta.

Bayan daukar tsawon lokaci ‘ya’yan majalisar na zaman sirri kan batun dawowar su ke da wuya suka amince da dokar.

Da ya ke Karin haske kan dokar shugaban masu rinjaye na majalisar Baffa Babba Dan-Agundi, ya ce, jikokin Sarki Dabo su za su ci gaba da sarautar masarautar Bichi haka zalika masu nadin sarautar Kano su zasu zabi Sarki a kasar Bichi.

Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Danbatta ya kalubalanci lamarin yana mai cewa ba a yi adalci wa arewacin Kano ba sakamakon cewa sarakuna uku daga cikin hudu sun fitone daga kudancin Kano.

Yayin da a bangare guda majalisar ta amincewa gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje da ya nada mai shari’a Nura a matsayin babban jojin jihar Kano.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!