Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

PRP zata daukaka kara kan hukuncin kotu ta yanke na sanata Uba Sani na jami’yyar APC

Published

on

Jam’iyyar PRP ta ce za ta daukaka kara kan hukuncin da kotun sauraran korafin zaben ‘yan majalisun dokokin tarayya na jihar Kaduna ta yanke game da kalubalantar nasarar da Sanata Uba Sani na jam’iyyar APC ya samu a yayin zaben da ya gabata.

 

A cewar jam’iyyar ta PRP ba ta gamsu da hukuncin da kotun ta yanke ba, a don haka za ta kalubalanci Matakin a kotu na gaba.

 

Da ya ke zantawa da manema labarai shugaban jam’iyyar a jihar ta Kaduna Alhaji Abdurrahman DanRimi, ya bayyana hukuncin a matsayin abin kunya wanda kuma jam’iyyar ba za ta amince da shi ba.

 

Tun farko dai kotun karkashin jagorancin mai shari’a A.H Suleiman a jiya Laraba ta yi watsi da korafin da Sanata Shehu Sani na jam’iyyar PRP ya shigar gabanta.

 

Kotun ta ce Sanata Shehu Sani ya gaza gamsar da ita cikakkun hujjojin da za su sa soke zaben.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!