Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Gwamnatin Kano za ta fara karrama ma’aikatan lafiya

Published

on

Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya umarci kwamishinan lafiya na jhar Kano Dakta Aminu Ibrahim Tsanyawa da ya fara karrama jajirtattun ma’aikatan lafiya da suka nuna kwazo wajen gudanar da ayyukansu.

Gwamna Ganduje ya ce wannan tsarin zai karawa ma’aikatan lafiya kwazo tare da bunkasa harkokin kiyon lafiyar a jihar Kano.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya bada umarnin  ne yayin bada takardar shaidar daukar aiki ga jami’an lafiya 920, inda ya ce Gwamnatin sa za ta ci gaba da tallafawa tsarin lafiya da kuma inganta shi.

Bayanin hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran Gwamnan Abba Anwar ya fitar.

Sanarwar ta kara da cewa, Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ya kuma tabbatar da cewa, inganta tsarin lafiya a matakin farko na daga cikin abin da gwamnatin sa za ta fi baiwa fifiko, don samar da ingantaccijyar al’umma, musamman ma a yankunan karkara.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya umarci sabbin ma aikata da su yi aiki tukuru da nuna kwarewa a wuraren da aka dauke su don bunkasa tsarin lafiya.

Rahotanni sun bayyana cewa, an dauki ma’aikata 626 karkashin hukumar kula da lafiya ta jiha, da kuma 294 karkashin hukumar kula da lafiya a matakin farko.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!