Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hukumomi sun gaza samar da mafita kan noman rani -Garba Gidan Maza

Published

on

Wani manomin rani daya shafe shekaru sama da arbain yana gudanarda Noma a Unguwar Gidan Maza a Kano Malam Garba Adali ya koka kan yadda har yanzu suka gaza samun cigaba a harkar noman rani musamman na rashin sabbin naurorin zamani sai dai suyi amfani da na gargajiya.

Garba Adall ya bayyana hakan ne a yayin zantawarsa da manema labarai yana mai cewa duk da irin yadda gwamnatin shugaba Buhari ke kokarin.

kamata ya yi a bunkasa harkar Noma amma ko kadan babu wani tallafi da suka taba samu daga gwamnatin tarayya a harkar noman su, a cewar Malam Garba Adali.

Gwamnatin tarayya ta yi yarjejeniya da shirin Sasakawa akan noma

Rikici ya barke tsakanin manoma da makiyaya a Kano

Gwamanti ta kebe fiye da bilyan goma don noman rani a Kano -Sani Bala

Malam Garba Adali ya kuma kara da cewa suna noma duk wasu nau’ikan kayan abinci, har ma da wanda turawa ke amfani da Su, amma matsalar rashin sabbin kayan zamani na noma nayi musu barazana sakamakon rashin karfin jarin da suke dashi.

Manomin ya kuma nanata cewa babbar matsalar da take ciwa manoman rani tuw0 a kwarya a yanzu bai wuce rashin takamaiman farashin kudin taki da suke fuskanta a wajen yan kasUwa ba. matukar ba kamfani aka je don siya ba, don haka akwai bukatar sanya hannun gwamnati.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!