Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Siyasa

Dai-dai ne kalaman Aisha Buhari –Shamsu Kura

Published

on

Wani dan siyasa a jihar Kano mai suna Shamsu Kura ya bayyana cewa kalaman da uwar gida shugaban kasa Aisha Buhari tayi gaskiya ne, domin kuwa batune da suka jima suna fadawa duniya cewa shugaban kasa ba shi ne yake mulkin kasar nan ba.

Yayin zantawarsa da Freedom Radio ta cikin shirin Kowane Gauta na ranar Larabar da ta gabata Shamsu Kura ya ce talakawan Nigeria Buhari suka zaba ba Mamman daura ko Garba Shehu ba.

A wannan makon da muke ciki ne dai uwargidan shugaban kasa Aisha Buhari ta aike da wata wasika ga jaridar Daily Trust wadda aciki ta bayyana cewa malam Garba Shehu da Mamman Daura suna yin shish-shigi a cikin ayyukan shugaban kasa.

Aisha Buhari ta ce Garba Shehun yana yin katsalandan hatta acikin al’amuran da suka shafi shugaban kasa da iyalansa, koda rufe ofishin matar shugaban kasa Mamman daura ne yabawa Garba Shehu umarni bawai umarnin shugaban kasa bane a cewar Aisha Buhari.

Labarai masu alaka:

Aisha Buhari ta nemi gafarar ‘yan Najeriya

Shin Aisha Buhari tayi yaji?

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!