Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Siyasa

Muna rokon gwamna Ganduje ya sulhunta Muntari da Sha’aban –Habib Sadam

Published

on

Daya daga matasan ‘yan siyasa na karamar hukumar birni da kewaye Habib Sadam Makwarari ya roki gwamnan jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje da ya sasanta manyan bangarori biyu na jami’iyyar APC a karamar hukumar.

A cikin shirin Kowane Gauta na nan Freedom Radio Habib Sadam ya bayyana cewa

“Ni dan karamar hukumar birni ne gaba dayan su ba inda babu dan uwana, ko ta auratayya ko ta musulunci ko ta zamantakewa, ba wanda ba dan uwana ba a ajiye maganar siyasa, wannan maganar za ta iya haifar mana da da mara ido”

Ya kara da cewa dukkan bangarorin dake da sabani da juna ‘yan uwana ne kuma ko babu siyasa cikin su za mu koma, a don haka yake rokon gwamnan ya yiwa Allah da ma’aiki ya shiga tsakanin bangarorin domin gudun kada rikicin ya rikide ya koma kan mallam talaka a cewar sa.

Rubutu masu alaka:

Dokar tsaftacce soshiyal midiya ba zata yi tasiri ba – Aminu Mai dawa

Muntari Ishaq ya can-can ci zama kwamishina -Aminu Mai dawa

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!