Labarai
Abubakar Malami ya zargi EFCC da yin amfani da karfin iko ba bisa ka’ida ba

Tsohon Ministan Shari’a na Najeriya Abubakar Malami, ya zargi hukumar EFCC da yin amfani da karfin iko ba bisa ka’ida ba, bayan da ya ce jami’an hukumar sun kwace gidaje da ofisoshinsa ba tare da umarnin kotu ba.
A wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Mohammed Bello Doka, ya fitar, Malami ya ce jami’an EFCC dauke da makamai sun mamaye kadarorinsa a safiyar Litinin, inda suka kama wasu mutane biyu.
Ya kara da cewa umarnin kotu na wucin gadi da EFCC ke jingina da shi ya riga ya kare, domin an bayar da shi ne na kwanaki 14 kacal tun a watan Janairu.
Tun da farko dai, kotu ta bayar da umarnin wucin gadi na kwace kadarori 57 da ake zargin suna da alaka da shi da ‘ya’yansa, yayin da kuma yake fuskantar tuhume-tuhume daban-daban daga EFCC da DSS
You must be logged in to post a comment Login