Connect with us

Labarai

Adamawa: Ƴan sanda sun cafke mutumin da ake zargi da yin garkuwa da mutane

Published

on

Rundunar yan sandan Jihar Adamawa, ta cafke wani mutum da ake zargi da yin garkuwa da mutane, da ke cikin jerin sunayen mutanen da ake nema ruwa a jallo a jihar.

Hakan na kunshe  cikin sanarwar da jam’in yaɗa labarai na rundunar ƴan Sandan Jihar ta Adamawa, SP Suleiman Yahaya Nguroje, ya fitar a jiya Lahadi.

Sanarwar ta tabbatar da  cewar  an kama  wanda ake zargin ne a Kasuwar Girei bayan samun  bayanan sirri, inda jami’an ’yan sanda suka kai samame suka kama shi.

A cewar sanarwar, daga cikin abubuwan da aka samu a hannunsa akwai kuɗi naira 100,000, gasassun kaji da sauran kayan abinci da darajarsu ta kai kimanin naira 230,000.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Adamawa, Dankombo Morris , ya yaba da ƙoƙarin jami’an da suka gudanar da aikin, tare da jaddada kudurin rundunar na ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!