Labarai
ADC ta zargi INEC da kitsa hanyoyin hana ta tsayar da yan takara a zaɓen 2027

Jam’iyyar ADC ta zargi hukumar zaɓe INEC, da shirya hanyoyin da za su hana ta tsayar da ‘yan takara a zaɓen 2027.
A cikin wata sanarwa da Sakataren yaɗa labarai na jam’iyyar,Malam Bolaji Abdullahi, ya fitar, jam’iyyar ta ce matakan da INEC ke ɗauka na iya hana ta shiga zaɓe gaba ɗaya, duk da cewa hukumar na cewa matakin na bin doka ne sakamakon shari’ar da ke gaban kotu.
Jaridar Daily Trust ta bayyana cewa rikicin ya samo asali ne daga matakin da INEC ta ɗauka na ƙin hulɗa da ADC har sai an kammala shari’ar shugabancin jam’iyyar a kotun tarayya.
Sai dai Jam’iyyar ta ce wannan mataki na barazana ga ikon ta na cika sharuddan doka, musamman wa’adin kwanaki 21 da dokar zaɓe ta tanada.
You must be logged in to post a comment Login