Connect with us

Kasuwanci

AFDB Na shirin tallafa wa fiye da manoma miliyan 2 a Nijar

Published

on

Bankin raya Ƙasashen Afirka AFDB, ya sanar da shirinsa na tallafa wa manoma sama da miliyan biyu a Jamhuriyar Nijar, don bunƙasa harkar noma a ƙasar.

Muƙaddashin mataimakin shugaban bankin na Martin Fregene ne ya sanar da hakan, a lokacin da ya ziyarci Fira ministan Nijar kuma ministan tattalin arzikin ƙasar Mahaman Ali Lamine Zeine, a birnin Niamey.

Fregene ya ce a ƙarƙashin tawagarsa da suka ziyarci Nijar, akwai kwararru a ɓangaren noma da tattalin arziƙi, waɗanda za su taimaka wajen tsara yadda za a samu nasarar shirin.

Ya ce suna fatan nan da shekarar 2027 za a ƙaddamar da shirin, wanda zai taimaka wajen cimma manufofin shugaban ƙasar Abdourahamane Tiani, na ciyar da ƙasar gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!