Connect with us

Labarai

Agege: Kwanan nan za ayi taron jin ra’ayin jama’a kan gyaran ƙundin tsarin mulki

Published

on

Majalisar dattijai ta ce tana shirye-shiryen gudanar da taron jin ra’ayin jama’a a dukkannin shiyyoyin kasar nan game da gyaran kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999.

 

A cewar majalisar tana son gudanar da taron jin ra’ayin jama’ar ne tsakanin ranakun 26 zuwa 27 ga watan da muke ciki na Mayu.

 

Mataimakin shugaban majalisar ta dattijai sanata Ovie Omo-Agege wanda shine shugaban kwamitin gyaran kundin tsarin mulkin mai kunshe da sanatoci 59 daga jihohin kasar nan 36 da birnin tarayya Abuja, shine ya bayyana haka ta cikin wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

 

Sanarwar ta ce, dukkannin sanatoci mata da sanatoci masu gafaka in ban da shugaban majalisar dattawa, suma mambobi ne a kwamitin

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!