Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ahmad Musa ya raba gari da kungiyar Al Nassr ta Saudia

Published

on

Kyaftin din kungiyar Kwallon kafa ta kasa Super Eagles Ahmed Musa , ya raba gari da kungiyar sa ta Al Nassr dake kasar Saudi Arabia , bayan shafe shekaru biyu a kungiyar.

Ahmad Musa ,wanda ya koma kungiyar a shekarar 2018 daga Leicester City , akan Kwantiragin shekaru hudu , ya sanar da barin kungiyar duk da ragowar Kwantiragin shekaru biyu da suka rage a yarjejeniyar sa da kungiyar.

Ita ma kungiyar ta Al Nassr, ta sanar da tafiyar dan wasan a shafinta na Twitter tare da cewa “Muna godiya Shahon Najeriya , muna maka fatan alheri a gaba”.

Sanarwar dai na zuwa ne , bayan da dan wasan mai shekaru 28, ya musanta labarin barin kungiyar a baya -bayan nan.

Ana Alakanta dan wasan da komawa tawagar Fenerbahce ta kasar Turkiyya (Turkey ).

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!