Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Al’amura sun tsaya cak a ma’aikatar ruwa ta Kano

Published

on

Al’amuran mulki sun tsaya cak a ma’aikatar samar da ruwansha ta jihar Kano, sakamakon rashin biyan ma’aikatan hukumar mafi karashin albashi da hukumar ta gaza biya tsahon watanni.

Da tsakar ranar yau juma’a ne dai fusatattun ma’aikatan hukumar suka garkame kofar shiga hukumar, babu shiga ba fita sakamakon rashin biyan su sabon mafi karancin albashi da suke ta faman jira a biya su.

Alhaji Shehu Lawan shine shugaban hadaddiyar kungiyar ma’aikatan ruwa reshen jihar Kano, a yayin zantawarsa da Freedom Radio ya bayyana cewa sun tara sama da naira miliyan Hamsin da Tara a amma biyansu albashi ya faskara sai dai ayi tayi musu alkawari.

“baki daya kudin da ake biyan ma’aikatan bai wuce naira miliyan sittin da daya ba amma biyan su ya faskara har izuwa yanzu” a cewar sa.

Alhaji Shehu Lawan ya kara da cewa abinda ya tunzura ma’aikatan daukar wannan mataki shine yadda aka biya su da tsohon albashin su na baya wanda yasa ma’aikatan na su suka tayar masa da hankali akan hakkin su.

Karanta karin labarai:

Mace ta zubawa dan kishiyarta ruwan zafi a Kano

Ma’aikatar ruwa sha ta kasa ta musanta zargin sayar da madatsan kasar

Freedom Radio tayi kokarin jin tabakin mahukuntan ma’aikatar ruwan ta jihar Kano amma abin yaci tura.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!