Connect with us

Labarai

Ali Ndume ya buƙaci shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya janye jerin sunayen jakadun da ya ke son nadawa

Published

on

Tsohon shugaban masu rinjaye na majalisar dattawan Najeriya, Ali Ndume, ya buƙaci shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya janye jerin sunayen jakadun da ke gaban majalisar a halin yanzu, bisa zargin cewa an saba wa ƙa’idar tsarin tarayya da kundin tsarin mulkin Shekarar 1999 ya tanada.

 

A ranar Alhamis ɗin da ta gabata ne majalisar dattawa ta karɓi jerin sunayen waɗanda shugaba Tinubu ke neman ya naɗa, waɗanda aka miƙa wa kwamitin majalisar dattawa kan harkokin ƙasashen waje domin tantance wa

Sai dai Ndume mai wakiltar Borno ta Kudu a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar ya ce jerin sunayen ya ci karo da sashe na 14(3) na kundin tsarin mulkin ƙasar nan wanda ya buƙaci a yi daidaito tsakanin ɓangarorin Najeriya wurin bayar da muƙaimai.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!