Labarai
Allah ya yi wa Mahmoud Madakin Gini rasuwa

Allah ya yi wa tsohon shugaban karamar hukumar Dala da ya yi tsawon zango biyu Mahmoud Madakin Gini, ya rasuwa.
Rahotonni sun bayyana cewa, Mmarigayin, wanda ya jagoranci karamar hukumar zamanin mulkin Sanata Ibrahim Shekarau a tsakanin shekarun 2004 zuwa 2011, ya rasu ne sakamakon hatsarin mota a garin Kateri yau Litinin a kan babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja.
Wata saarwa da shugaban karamar hukumar Dala Surajo Ibrahim Imam, ya fitar ta ce, za a gudanar da jana’izarsa da misalin karfe 5:00 na yamma a gidansu da ke unguwar Yelwa.
You must be logged in to post a comment Login