Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Al’ummar unguwar Shekar Mai daki sun yi tayin gidajen su ga Dagaci

Published

on

Mazauna unguwar Shekar Mai daki dake karamar hukumar Kumbotso a nan Kano, sun yi tayin gidajen su ga dagacin yankin Malam Badamasi Muhammad.

Tayin ya biyo bayan kin jinin sababbin zuwa unguwar da suke zargin dagacin na yi.

Wasu mazauna unguwar sun shaidawa Freedom Radio cewa dagacin yana nuna musu kyama da wariya a matsayin su na baki, wadanda suka mallaki gidaje a wurin ba ‘yan asalin yankin ba.

Har ila yau, sun ce dagacin na taka rawa wajen dakile musu damarmaki da suke samu.

Wakilin mu Yusuf Ali Abdallah ya garzaya har gidan dagacin domin jin ta bakin sa amma ya ce a bashi lokaci, zuwa karfe biyar na yamma.

Kuma wakilin na mu yayi kokarin jin ta bakin dagacin a lokacin da ya bayar amma abin ya gagara.

Karin labarai:

Dagaci ya gano maboyar batagari a Kano

‘Yan garkuwa sun sace dagaci a Kano

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!