Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ambaliyar ruwa ta shafi jihohin Najeriya 12- hukumar NEMA

Published

on

Hukumar bada agajin gaggawa ta kasa NEMA ta ayyana jihohin kasar nan goma 12 da ke rayuwa a gabar kogin Niger da Benue a matsayin wadanda iftila’in ambaliyar ruwa ya shafa fiye da sauran jihohin kasar nan.

Shugaban hukumar ta NEMA Alhaji Mustapha Maihaja ne ya bayyana hakan yayin taron hukumar na wata-wata da zauren masu lura da al’amuran tsaro da jami’in yada labaran hukumar ke gudanarwa.

Ya ce tuni aka kididdige irin asarar da aka yi a mafi yawa daga cikni jihohin kasar nan da suka samu mamakon ruwan sama a bana, da ya yi sanadiyyar kogunanan Niger da Benue suka yi ambaliya.

Ya kuma ayyana sunayen jihohin Benue da Kogi da Niger da kuma Kwara sai jihar Anambra da Benue da Delta da Bayelsa da Rivers sai kuma Adamawa da Kebbi da Taraba a matsayin wadanda suka fi sauran jihohin kasar kamuwa da wannan iftila’i.

A cewar Mustapha mai Haja matakin da aka dauka tun da fari kafin aukuwar al’amarin shi ne ya taimaka wajen dakile yawaitar matsalar kamar yadda ya faru a shekarar 2012.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!